Mataimakin shugaban kungiyar hadin kan kungiyoyi masu zaman kansu dake kula da dokokin hanya Yusuf Zubairu ya bukaci gwamnatin tarayya da ta aiwatar da tsarin Majalisar Dinkin Duniya na shekarar 2021 zuwa 2030 don kiyaye hadurra a fadin kasar nan.
Ya ce hakan zai taimaka wajen samar da hanyoyin da ba su da hadari da kuma kiyaye asarar rayuka.
Ya yi wannan jawabi ne a karshen makon da ya gabata a Abuja, lokacin da kungiyar mata masu kula da hanyoyin kiyaye hadurra (ROSOWA) ta ziyarci asibitin Garki domin bayar da gudummawar kayayyaki ga wadanda abin ya shafa a kan tituna a wani bangare na gudanar da bukukuwan tunawa da ranar tunawa ta duniya ga wadanda abin ya shafa.
Zubairu ya bayyana rashin gudun wuce kima, a matsayin maganin hadarurruka.
Ya dorawa gwamnati alhakin bayar da shawarwari tare da hukunta masu laifi.
Daraktan ayyuka da ayyukan jinya na asibitin Garki, Dakta Kenneth Ityo, ya ce asibitin na kula da wadanda abin ya shafa da zarar an kai su asibitin.