Daga Khadija Mohammed Kano
Daya daga cikin masu garkuwa da mutane wanda aka kama Dan shekaru ashirin da takwas yace ya shiga cikin wannan laifin ne tun Shekaran dubu biyu da sha biyar (2015) Dan ya samo kudin da zai karasa biyan lauyansa.
An kama masu laifin sanya da kayan sojojji na bogi.
Mutumin ya jagoranci jami’an tsoro wajen damke sauran masu laifin su uku wanda ya Hadar da Daniel Johngbo, Harridon barriers, da lebara Tobia wadanda aka kama su a wurare daban daban na jihar.
Locakin da ake yi wa daya daga cikin masu garkuwa da mutane mai suna apollolos ya bayyana cewa sunyi garkuwa da wata dattijuwar Mata mai kimanin shekaru 67 a duniya yar kasuwa mai suna Obianuju.
Sun bayyanawa jami’an tsaro cewan sunyi garkuwa da matar sanda take kan hanyar ta na dawo daga chochi acikin wata Mota kira Toyota sienna Ranar 7 ga watan mayu na wannan shekaran, inda suka tsare Mata hanya kusa da gidan ta har sai da ta tsaya sannan suka kamata suka sanya ta a motar su suka tafi da ita.
Bayan da suka kamata sun ajiye ta a wani daji inda suka bukaci a tura musu magwudan kudade na miliyoyi, wanda kuma aka basu sannan aka sako ta.
Bayan da ta fito ne shine ta sanar da shugaban hukumar yan sanda mai suna inspecta janaral Mohammed Adamu, shi kuma ya bada umarnin a damko su duk inda suke a fadin kasar.
Apollolos ya yi karin bayani cewan wani mai suna Gbenena shi ya shirya ya kuma tsara yadda zasu yi garkuwa da matar wanda har yanzu ba a kamo Shi ba. Apollolos ya bayyana cewan ya samu dubu dari uku da hamsin (350,000) amatsayin nashi kason daga cikin miliyoyin da yan uwan matar suka biya su.