• Harin kwantan bauna a ka Kai wa jami’an a wani gari da ke arewacin kasar.
• Jami’an yan sandan kasar 11 ne suka mutu sanadiyar harin, inda 4 su ka bace.
• Ministan harkokin tsaron kasar ya tabbatar da afkuwan lamarin a wata sanarwa da ya fitar a jiya.
Gwamnatin kasar Burkina Faso ta ce, an kai wa jami’an yan sandan kasar hari, a arewacin kasar, wanda ya yi sanadiyar mutuwar jami’an ta 11, inda kuma 4 su ka bace.
A cikin wata sanarwa da Ministan harkokin tsaron kasar Ousseini Campaore ya fitar a jiya Talata, ta ce, ” an kai wa jami’an hari ne, lokacin da su ka je kwantar da tarzoma a yankin Yirgou, garin da ke fama da rikice-rikice.
KARANTA WANNAN LABARIN: Majalissar dattijai ta amince da nadin Manjo janar Faruk Yahaya
Sai dai haryanzu babu wata kungiyar da ta dauka nauyin harin, amma tun a shekarar 2015 kasar ta Burkina Faso ke fama da kokarin dakile hare haren wasu kungiyoyi da ke da alaka da kungiyar Al-Qaeda da kuma ISIS.
Kazalika tun a shekarar 2019, “Rikice-rikicen da kasar ke fama dashi ya yi sanadiyar barin mutun milliyan daya, da dubu dari biyu, daga gidaje su” a cewar hukumar kula da masu gudun hijira ta majalissar dinkin duniya.
Kuma Rikice-rikicen kasar ya sa mutun 150,000 barin gidajen su, a wannan shekarar kadai.inji hukumar ta MDD, inda ta kara da cewa, kaso 84 cikin100 mata ne.