Hukumar ba da agaji gaggawa ta kasa wato NEMA a jiya Alhamis ta sake karbar wadansu ‘yan Nijeriyar guda 141 wadanda aka dawo da su daga kasar Libya.
Alhaji Abubakar Muhammed, Kodinetan NEMA din a Legas, shi ne ya karbi ‘yan Nijeriyar a madadin gwamnatin tarayya wadanda aka bar su yashe a Libya. Sun sauka a sashen Cargo na filin jirgin Murtala Muhammed dake Legas.
Muhammed ya shaidawa manema labarai cewa; ‘yan Nijeriyar sun dawo ta cikin Al Buraq Air Plane mai lamba UZ389/24 da kuma lamba 5A-DMG da misalin karfe 4:32 na yamma.
Ya tabbatar da cewa sun dawo ne bisa taimakon EU, IOM a wani mataki na dawo da ‘yan Nijeriya gida, inda ya ce daga shekarar 2017 da aka fara dawo da ‘yan Nijeriyar da aka bar su yashe, yanzu haka an dawo da mutum dubu 15.