By Abbas Yakubu Yaura
A halin yanzu dai ana ci gaba da yin wasan kwaikwayo a zauren majalisar dokokin jihar Kogi yayin da ‘yan majalisa 19 suka yi ikirarin tsige shugaban majalisar, Matthew Kolawole.
Lamarin ya zo ne sa’o’i kadan bayan sallamar Ahmed Muhammed a matsayin mataimakin kakakin majalisar da wasu manyan jami’ai uku da ‘yan majalisa 17 suka yi.
KARANTA WANNAN LABARIN: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Sakataren Hukumar NFA, Sani Toro Da Karin Wani mutum Guda
Wata wasika da aka rabawa manema labarai a Lokoja, babban birnin jihar a ranar Asabar din da ta gabata, ta nuna cewa ‘yan majalisa 19 ne suka rattaba hannu a kan takardar ta tsige shugaban majalisar.
‘Yan majalisar da suka rattaba hannu kan takardar sun yi ikirarin cewa an tsige shugaban majalisar ne bisa zargin aikata ba daidai ba da kuma karkatar da makudan kudade na miliyoyin naira.
A cewar ‘yan majalisar, korar Kolawole ta fara aiki ne tun daga ranar Litinin, 13 ga watan Yuni, 2022.
‘Yan majalisar 19 sun zayyana laifukan Kolawole da suka hada da rashin biyan ‘yan majalisar hakkokinsu na tsarin mulki, da cin hanci da rashawa da kuma karkatar da kudaden da aka ware wa majalisar tun daga shekarar 2019.
Sun kara da cewa shugaban majalisar ya samu lamuni na kashin kansa, inda ya yi amfani da asusun majalisar wajen cutar da sauran mambobin majalisar.
‘Yan majalisar da suka fusata sun ci gaba da zargin cewa Kolawole ya nakasa mutuncin ‘yan uwa ta hanyar rubuta tarurruka da hirarrakin ‘ya’yan kungiyar tare da yin amfani da su wajen bata masu suna domin samun tagomashi a wurin gwamnan jihar, Yahaya Bello.
Da aka tuntubi Babban Sakataren Yada Labarai na Shugaban Majalisar, Femi Olugbemi, ya bayyana korar Kolawole a matsayin wani tunanin ‘yan majalisar da abin ya shafa.
Ya ce Kolawole ya ci gaba da zama shugaban majalisar, ya kara da cewa duk wata harka ta majalissa da ba a yi a zauren majalisar ba ya sabawa doka.
Ya ce, “Ta yaya za ku yi iƙirarin tsige Shugaban Majalisar ba tare da wanda ya maye gurbinsa ba? Ba za a iya samun wurin ba.”