Allah ya yiwa Alhaji Sa’ad Mainasara rasuwa yana da shekara 58 a duniya. Marigayin shi ne Hakimin garin Tambuwal, garin gwamnan jihar Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal.
Ya rasu ne da misalin karfe 9 na daren ranar Alhamis a wani asibiti mai zaman kansa a birnin tarayya Abuja bayan ya yi fama da rashin lafiya.
Marigayin ya rasu ya bar mata biyu, da ‘ya’ya tara, maza bakwai, mata biyu. Inda aka yi jana’izarsa a ranar Juma’a a garin Tambuwal da misalin karfe 2:30 na yamma.
Shamakin Tambuwal, Muhammadu Bello a yayin da yake bayyana dabi’un marigayin, ya bayyana shi a matsayin mutum mai addini, kuma mutumin kirki, kuma shugaba mai hangen nesa da koyaushe al’ummarsa ce a zuciyarsa.
Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da tuna Marigayin a matsayin mutum jajirtacce wanda ya tsayawa al’ummarsa.
Dan’uwan Hakimin, Almustapha Dahiru, ya bayyana cewa dan uwan na sa a matsayin tsohon ma’aikacin lafiya, ya bada gudummawa sosan gaske wajen yaki da cutar foliyo da sauran cutuka masu kashe kananan yara.