Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, a halin yanzu kasar nan ta samu karin zaman lafiya a dukkan sassan kasa, musamman a daidai lokacin da muka shiga watannin karshe na shekara.
Shugaban rundunar ‘yan sandan Nijeriya, Muhammed Adamu, ya bayana haka bayan da aka kammala taron majalisar tsrao ta kasa wadda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta a Abuja yau Talata.
Ya ce, taron da aka yi ya tattauna tare da nazarin harkar tsaro a kasar, an kuma lura cewa, lallai an samu kari zaman lafiya a kasar.
Ya kuma kara da cewa,“Taron ya lura da cewa, an samu raguwar garkuwa da mutane a sassan kasar gaba daya.
“Wuraren da aka fi samu garkuwa da mutane irin su arewa maso yammancin kasar nan, kamar jihar Zamfara da Katsina da Kaduna duk sun samu zaman lafiya ba kamar da ba.
“Ta’addanci da ake yi a yankin arewa maso gabas ya yi matukar raguwa, an ci galabar ‘yan ta’adda, wasu kuma daga cikinsu sun yi saranda tare da mika wuyarsu, wannan lallai abin alfahari ne kwarai da gaske.
“Dukkan wannan nasara ne da aka samu ya faru ne sakamakon goyon bayan da aka samu daga al’umma, muna kuma fatan ci gaba da samun wannna goyon bayan.’’