Kwamitin ayyuka na jam’iyyar APC a mazabar Rumde na karamar hukumar Yola ta Arewa ya dakatar da mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa a yankin (Arewa-maso-gabas) Kwamared Mustapha Salihu na tsawon watanni shida, bisa zarginsa da aikata cin amana, Tribune Online ta rawaito.
Haka kuma an dakatar da shugaban jam’iyyar na gundumar Abdulkadir Abdullahi.
KARANTA WANNAN LABARIN: Gwamnatin Zamfara Ta Dauki Jami’an Yaki Da ‘Yan Daba 2,500
An bayyana dakatar da ‘yan biyun ne a wata sanarwa ta daban a ranar Lahadin da ta gabata tare da sanya hannun mataimakin shugaban jam’iyyar APC na yankin mazabar Rumde, Abdulhadi Ahmed, da Sakatare, Garba Mohammed da wasu shuwagabanni 16.
A halin da ake ciki kuma, dakatarwar da aka yi wa shugabannin biyu a matakin Unguwanni an ce an mika shi ga mukaddashin shugaban jam’iyyar APC na jihar Adamawa da kuma shugaban jam’iyyar na karamar hukumar Yola ta Arewa.
Wasikar dakatarwar Salihu ta ce: “Kwamitin ayyuka na jam’iyyar APC,na mazabar Rumde, reshen karamar hukumar Yola ta Arewa sun gudanar da taron gaggawa a ranar Lahadi 19 ga watan Fabrairu, 2023 tare da la’akari da wasu abubuwa da dama da ke gabanta, da dakatar da Mataimakin shugaban jam’iyyar APC na yankin arewa maso gabas, Kwamared Mustapha Salihu,nan take kan fallasa da kuma tabbatar da ayyukan da suka saba wa jam’iyyar, da cin zarafin mukamai da kuma haifar da rikici a cikin jam’iyyar a dukkan matakai wanda idan ba a daidaita su ba zai shafi jam’iyyar a babban zabe mai zuwa.
“Saboda haka, bisa bin ka’idojin da suka dace na kundin tsarin mulkin babbar jam’iyyarmu, mambobin kwamitin aiki sun amince da dakatar da Comrade Mustapha Salihu na tsawon watanni shida da gaggawa ta yadda zai zama abin hana wasu a gaba
“Wannan kwamiti yana sane da irin nauyin da ya rataya a wuyan jam’iyyar kuma koyaushe zai tabbatar da daukakar jam’iyyar sama da duk wata maslaha ta kowane mutum ko gungun mutane musamman a lokacin da hakan ke kawo hadari ga damar jam’iyyar a zabe.
“Yayin da muke godiya ga kwamitin Ayyuka na jam’iyyarmu na jiha bisa ci gaba da goyon bayan ku, muna fatan shawararmu za ta sami hanzari.”
A wani labarin kuma, APC Ta Tafka Asara Ya Yin Da Mambobinta Suka koma PDP
’Yan jam’iyyar APC a shiyyar Enugu ta yamma sun sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP domin marawa dan takararta na gwamna Barista Peter Mba baya.
‘Yan jam’iyyar APC sun kona tsintsiya madaurinki daya a lokacin da suke rungumar jam’iyyar PDP a wajen taron amincewa da aka shirya a shiyyar.