By Abbas Yakubu Yaura
Mataimakin gwamnan jihar Gombe, Dakta Manassah Jatau, a ranar Laraba ya koka da yadda ake samun karuwar auren yara mata a cikin al’ummar Konfulata dake karamar hukumar Kwami a jihar.
Jatau ya bayyana takaicin sa kan yadda ake kara samun karuwar ciki na samari, wanda yace ya zama ruwan dare a tsakanin al’umma.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa mataimakin gwamnan yayi wannan jawabi ne a lokacin daya karbi bakuncin shugabannin al’ummar Gadam da suka zo neman hanyar shiga da kuma ziyarar godiya bayan rufe asusun kula da kananan yara na UNICEF, da taimakon gwamnatin kasar Sin ga cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko guda 10 a yankin.
A cewarsa, UNICEF da gwamnatin kasar Sin sun yi alkawarin yin la’akari da ci gaban da aka samu wajen gudanar da aikin, bayan da aka samu nasarori masu yawa, da mayar da martani da kuma goyon baya daga jama’ar yankunan da abin ya shafa.
Mataimakin gwamnan ya yi amfani da damar wajen yin rijistar damuwarsa kan auren wuri da daukar ciki na Kananan yara mata. Sannan yace, “An lura da auren wuri da yin ciki a ziyarar da suka kai Konfulata kwanan nan.
“Yayin da muke kokarin samar da kiwon lafiya, ya kamata mu yi taka tsantsan kada mu bar abin da zai jefa rayuwar jama’a cikin hadari.”
Jatau ya sanar dasu cewa yawancin bukatunsu na cikin shirye-shiryensu kuma tuni aka gabatar dasu a gaban gwamna.Na tabbatar musu da amsa mai kyau.
Kazalika ya yaba da shirin samar da sana’o’i na kungiyar ci gaban al’ummar Gadam ga matasansu da mata, inda ya nuna cewa hakan zai taimaka matuka wajen yaba kokarin gwamnati na karfafa matasa.