Shugaban Jam’iyyar APC, Adams Oshiomhole ya bayyana cewa a shekaru uku da gwamnan jihar Kogi wato Yahaya Bello ya yi yana mulkin jiharsa, ya yi gagarumin aikin da jam’iyyar PDP ma ba ta iya yi ba a tsawon shekaru 16 da ta yi tana mulki a jihar.
Oshiomhole ya bayyana hakan ne a yayin da yake ganawa da gwamna Yahaya Bello a hedikwatar jam’iyyar APC a birnin tarayya Abuja.
Oshiomole ya ce; Yahaya Bello ya cika haifaffe a jihar Kogi domin kuwa ya yi abin da ba a taba yi ba a jihar a tsawon mulkin Jam’iyyar PDP. Ya kara da cewa; Ka da a manta cewa tarin albashin ma’aikatan jihar da ba a iya biya ba gadarsa ya yi daga gwamnatin baya, wato gwamnatin PDP.
Sannan ce; kuma baya ga tarin albashi da ba a biya ba, tsaro ya tabarbare a jihar da hakan yasa ake ta fama da tashin hankula a tsakanin mutanen jihar. Sai gashi yanzu komai ya lafa. Tsaro ya kankama saboda kokari da maida hankali da gwamnan ya yi wajen ganin ya dawo da zaman lafiya a jihar.
Baya ga haka Oshiomhole ya ce tuni har uwar jam’iyyar ta sasanta duka wadanda ba su ga maciji a tsakaninsu a jam’iyyar. Sannan kuma tuni har an shirya ‘yan takarar da ba su yi nasara ba a zaben fidda gwani da gwamnan jihar.