Kwamishinan yada labaran Jihar Kano Mallam Muhammad Garba ya ce hoton dake ta yawo a kafafen sada zumunta na zamani dake nuna gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar ke taka hoton tsohon gwamna Rabiu Musa Kwankwaso ba da gangan ba ne.
Al’amarin dai ya faru ne a ranar Asabar yayin gangamin bikin ranar dimokuradiyya tare da tarbar wasu yan jam’iyyu daban-daban da suka sauya sheka zuwa APC.
Wata sanarwa da Kwamishinan ya fitar, ta ce babu wani rashin jituwa ko kiyayya da za ta sanya gwamna Ganduje nuna rashin ɗa’a wa wani dan siyasa ko wanene, domin ba dabi’arsa ba ce.
Sanarwar ta kara da cewa wasu marasa kishi ne kawai ke kokarin amfani da wannan dama wajen samun na abinci, don haka dole ne a yi la’akari da alaka dake tsakanin mutanen biyu don gudun kawo ruɗani a hidimar siyasar jihar.
Mallam Muhammad Garba ya ce al’amarin ya faru ne daidai lokacin da gwamna Ganduje ya tashi zuwa jawabi a kan kanta, yayin taron ranar dimokuradiyya ta Najeriya da jihar ta bi sahun Jihohin kasar nan.
“Abinda ya faru shine, kamar yadda kowa ya sani akwai yan akidar darikar Kwankwasiyya da suka sauya sheka, ciki har da wasu da suka nemi tsayawa takarar gwamnan jihar”
“Sa’in da aka bukaci gwamna Ganduje da ya taso ya yi jawabi, daga cikin magoya baya daya sai hoton Kwankwaso ya faɗi a hannunsa daidai lokacin gwamnan yana tafiya zuwa kan kanta don yi jawabi”
“Shi bai ma lura da cewa akwai hoto a gurin ba ballantana ya san ko na wanene” cewar Sanarwar ta Garba.
Daga bisani dai sanarwar ta jaddada cewa matakin Gwamna Ganduje na son zaman lafiya da kaunar juna yana nan, don haka ba za a bari wasu tsiraru su yi yunkurin tada zaune tsaye ba.