Gwamnatin tarayya ta gayyaci masu shiga tsakani na kasashen Amurka da Birtaniya da Kanada da kuma na tarayyar turai da su gurfana a gabanta.
Wannan kira ya biyo bayan ɓaɓatu ne da wadannan mutane suka yi kan haramta tuwita da gwamnatin tarayya ta yi a ranar Juma’a.
Dukkannin waɗannan kasashen na duniya sun yi tir da wannan mataki, inda suka ayyana hakan a matsayin tauye hakkin dan Najeriya.
Wata Sanarwa da shugaban sashen kula da rikice rikice a ofishin ma’aikatar harkokin wajen Najeriya Kimiebi Abienfa ya fitar, ta bukaci jagororin kasashen da su gaggauta zuwa don tattaunawa da Ministan Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya Geoffrey Onyeama.