Ministan matasa da ci gaban wasanni, Sunday Dare ya tabbatar da cewa samar da ayyukan yi ga matasa da kuma karfafa musu guiwa yana daya daga cikin manyan kudurorin shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Dare ya tabbatar da hakan ne a wata sanarwa da Patricia Nnandi, jami’in labarai na ma’aikatar ta sanyawa hannu, inda ya ce gwamnati tana iya bakin kokarinta wajen ganin ta tallafawa matasan Nijeriya a fannin ilimi, lafiya, fasaha, kimiyya, siyasa da kuma shugabanci.
Ta tabbatar da cewa ministan ya bayyana hakan ne a yayin da membobin kungiyar ‘United Northern Youth Students’ suka kai masa ziyara a birnin tarayya Abuja.