Babban bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana cewa ya tsara bai wa manoma tare da kananan yan kasuwa kimanin 70, 000 bashi, a karkashin shirin ta na bayar da lamuni na :Anchor Borrower Programme’ (ABP) a jihar Borno cikin wannan shekara ta 2019.
Bayanin hakan ya fito ne daga babban jami’in kula da sashen Finance Debelopment Office (DFO) a bankin CBN, Mahmood Nyako, a lokacin da yake tattauna wa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a Maiduguri, banban birnin jihar, a karshen mako.
Mista Nyako ya kara da cewa bankin CBN ya shirya aiwatar da muhimman tsare-rsare masu ma’ana don bunkasa samar da kayan amfani tare da sake fasalin tsara hanyoyin karfafa gwiwar abokan hulda, farfado da tsarin tattalin arzikin jama’a da bunkasa kanana da matsakaitan masana’antu (SMSE).
Nyako ya ayyana wasu daga cikin shirin da bankin CBN na bayar da lamunin, sun kunshi; tsarin habaka ci gaban sha’anin noma, tsarin gidauniyar ayyukan noma da bai wa manoma lamuni, tare da fannin kasuwancin kanana da matsakaitan kayan gona da makamantan su.
Haka kuma ya shaidar da cewar, kimanin mutum 52, 008 za su gajiyar wannan shirin lamuni, tare da karin manyan manoma 500 a karkashin lemar kungiyar ACGSF da matasa 17, 000 hadi da kananan yan kasuwa a karkashin AADS, AGSMEIS za su ci gajiyar wannan shirin.
Bugu da kari kuma, babban jami’in ya ce, bankin ya yi rijistar kungiyoyin manoma guda takwas tare da na yan kasuwa masu cin gashin kan su da na bayar da lamuni wajen karfafa gwiwa don samar da isassun kayan abinci ga manoman rani a karkashin shirin lamunin.
“Bankin CBN ya samar da naira biliyan 2 don aiwatar da wannan shirin; Paddy Aggregation Scheme (PAS) da Maize Aggregation Scheme (MAS), wajen bunkasa tsarin. Kudaden an tsara yin amfani da su wajen sake farfado da aikin noma, inganta shi tare da habaka kasuwancin ayyukan noma”. In ji shi.
Har wala yau kuma, Mista Nyako ya kara da cewa, akwai karin wasu naira biliyan 1.5 ne bankin ya ware zuwa ga gwamnatin jihar, don bude filin noma mai fadin kadada 10, 000 yayin da bankin zai jagoranci raba kayayyakin.
A hannu guda kuma jami’in ya yi kiran bai-daya ga gwamnatin jihar hadi da na kananan hukumomi, wajen kokarin fadakar da kan jama’ar su wajen shiga cikin shirin, sannan kuma ya bukaci wadanda za su ci gajiyar tsarin da cewa su yi amfani da kudin lamunin don habaka rayuwarsu