A kalla Likitoci takwas ne suka kamu da cutar Corona Virus a Jihar Zamfara, kamar yadda kungiyar Likitoci reshen jihar ta bayyana (NMA).
Hakan ya fito ne daga bakin mataimakin kungiyar Dakta Mannir Bature, yayin da yake tattaunawa da manema labarai a ranar Laraba, a garin Gusau.
“A yanzu haka muna da mutane sama da 80 wanda suka kamu da cutar wanda kaso 10 daga cikinsu Likitoci ne, kuma sun kamu ne sakamakon hulda da suka yi da masu dauke da cutar a yayin nema musu lafiya”.
“Amma muna cike da farin ciki sakamakon yadda masu dauke da cutar ke warkewa akan lokaci. Yanzu haka an sallami kaso 60 daga cikinsu, kuma muna fatan sake sallamar wasu nan gaba kadan”.
Dakta Bature ya kara da cewa, Likitoci 30 da suka yi hulda da masu dauke da cutar COVID19 sun killace kansu.
“Yanayin da ake ciki ya karyar mana da guiwa saboda karancin Likitoci da muke fama da su a jihar nan, gaba dayanmu bamu wuce mu 300 ba duk da wanda suke karkashin gwamnatin tarayya, da kuma wanda suke aiki a asibitoci masu zaman kansu”.
“Shi yasa a matsayinmu na kungiya muka mika kokenmu ga gwamna Bello Matawalle, domin a kawo mana agaji wajen karo mutanen da suka karanci harkar lafiya tare da dabilan kiwon lafiya a jihar nan domin samun damar kawo karshen wannan annoba ta Corona Virus a jihar nan”.
Daga: Abubakar Muhammad Usman