Rahotanni sun tabbatar da cewa wasu bata gari yanzu haka, sum sace Tsohon janar manajan hukumar kula da tashoshin ruwa na tarayya Bashir M Abdullahi.
Yan garkuwar dai sun sace Abdullahi a gonarsa dake kauyen Gomo a yankin karamar hukumar Sumaila a yammacin yau Laraba.
Mazauna kauyen na Gomo sun ce yan bindiga sun dauke tsohon babban manajan hukumar lokacin da yake gonarsa domin rangadi.
Yayin da muka tuntubi mai magana da yawun rundunar yan sandan Kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya ce basu da masaniya kan faruwar lamarin, amma zasu bincika kuma da zarar sun kammala zasu yi karin haske.
Comments 1