Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri na jihar Adamawa ya zabi mace Farfesa Kaletapwa Farauta a matsayin mataimakiyarsa a zaben 2023.
A halin yanzu Farfesa Farauta ita ce Mataimakiyar Shugaban Jami’ar Jihar Adamawa da ke Mubi.
A wajen bikin kaddamar da ita a Yola ranar Laraba, Fintiri ya ce an zabi Farfesa Farauta ce bisa gaskiya, rikon amana, da kuma kwazon da take nunawa akan aiki.
Ya ce ana sa ran za ta sauke nauyin da ke kanta tare da taka tsantsan da tsoron Allah, baya ga aikin da take ta yi na uwa na kula da gida.
KARANTA WANNAN LABARIN: Sanatoci Sun Shiga Ganawar Sirri Da Shugabannin Tsaro, Ana Tsaka Da Barazanar Tsige Buhari
“Zabar ta ya samo asali ne sakamakon korafe-korafe da kuma kididdigar dabaru musamman bukatar kara daukar matan ta hanyar kula da kuma yiwa kowani jinsi adalci in ji shi.
Gwamna Fintiri ya bukaci jam’iyyun adawa da su shiga cikin gwamnatinsa domin ci gaban jihar.
A nata jawabin, Misis Farauta, wadda ta bayyana zaben ta a matsayin wani abin da Allah ya yi, ta godewa Mista Fintiri da kuma jam’iyyar PDP da suka same ta a matsayin wanda ta cancanta.
Yayin da take ba da tabbacin yin hidima cikin aminci, jajircewa, sadaukarwa da kuma tsoron Allah, ta kuma ce : “Za mu yi aiki tukuru don tabbatar da nasarar jam’iyyar mu a duk zabukan da za a yi nan gaba”.
Mrs Farauta, an haife ta ne a ranar 28 ga watan Nuwamba, 1965 a karamar hukumar Numan, ƙwararriyar fasaha ce wadda ta zama mataimakiyar shugabar mata ta farko a yankin Arewa maso Gabas a Jami’ar Jihar Adamawa dake garin Mubi.