Rundunar ‘yan sandan Najeriya reshen jihar Taraba ta tabbatar da mutuwar Bassy Sardauna, malamin makarantar sakandare da dalibai suka kashe a ranar Laraba a Jalingo.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis, mai magana da yawun rundunar, Abdullahi Usman, ya ce marigayin ma’aikacin makarantar Model Secondary School ne, Jalingo.
Karanta nanNijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Wata Yarjejeniyar Makamashi
A cewarsa, wanda ake zargin wanda ya bayyana a matsayin tsohon dalibin makarantar, ya hada baki da abokansa a makarantar, inda suka daba wa malamin wuka, wanda aka tabbatar da mutuwarsa a babban asibitin tarayya da ke FMC a Jalingo, inda aka kai shi. domin magani.
Usman ya tabbatar da cewa rundunar ta fara bincike kan lamarin idan suka kammala bincike za su sanar da ‘yan jarida.
Rundunar ‘yan sandan ta tabbatar da cewa, ana ci gaba da kokarin zakulo dukkan daliban da ke da hannu a kisan, ya kuma bukaci duk wanda ke da wani bayani game da inda suke da ya tuntubi rundunar.
A wani labarin kumaYakin Ukraine Da Rasha Ya Taba Tattalin Arzikin Nijeriya–Akpabio
Binciken DAILY POST ya nuna cewa harin da aka kai wa marigayin ya biyo bayan matakin da ya dauka na hukunta wasu dalibai a makarantar kwanan nan. Wasu daga cikin daliban da suka dade suna harin malamin sun yi masa kwanton bauna a hanyarsa ta komawa gida.
Duk da cewa har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto ba a iya samun mahukuntan makarantar, wasu ma’aikatan makarantar da suka tabbatar da faruwar lamarin sun yi zargin cewa munanan dabi’un wasu daliban musamman wadanda ke manyan ajujuwa,yasa suka aikata wannan abin.