Dalilin Da Ya Sa Na Ba Da Umarnin Kama Ɗan Majalisar Bauchi – Kwamishinan Ƴan Sanda
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Aminu Alhassan, ya bayyana dalilin da ya sa ya bayar da umarnin damke dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Bauchi a majalisar wakilai, Hon Yakubu Shehu, Abdullahi.
A ranar Talata ne rundunar ‘yan sandan ta bayyana dan majalisar tarayya da ake nema ruwa a jallo bisa zarginsa da laifin hada baki, dagula zaman lafiyar jama’a da kuma kisan kai.
KARANTA WANNAN LABARIN: Gwamnan Borno: Ƙungiyar CAN ta Musanta Amincewa Da Ɗan Takarar PDP
Da yake zantawa da manema labarai jiya Laraba a ofishin sa yayin da yake mayar da martani kan zargin da tsohon kakakin majalisar wakilai Yakubu Dogara ya yi na cewa rundunar ‘yan sanda ba ta bi ka’ida ba wajen bayar da umarnin kama shi, CP Alhassan ya ce dan majalisar ba shi da hurumin kama shi bisa zargin aikata laifukan da ake tuhumarsa da shi.
Kwamishinan ‘yan sandan ya ce bayan rikicin da ya barke a garin Duguri da ke mahaifar gwamnan a karamar hukumar Alkaleri wanda ya yi sanadin mutuwar mutum daya tare da jikkata wasu 15, ‘yan sandan jihar sun fara bincike.
Kwamishinan ya bayyana cewa, “Lokacin da muka ji cewa wani ya mutu kuma yana nuna wasu fitattun mutane hudu a cikin wannan kungiyar, sai muka fara nemansu, a gaskiya daya daga cikin hanyoyin da ya fi saurin samun bayanai, ita ce fara magana da su masu ruwa da tsaki. Na shaida wa jam’iyyar APC cewa zan bukaci akalla manyan masu ruwa da tsaki guda biyu a jihar kuma sun tabbatar min da cewa za su zo.
“Da magariba sai na tuntube su ta wayata, har ma na aika musu da sakon cewa wadannan mutane ne da nake bukata saboda zargin da ake yi, har na aika da hotunan zargin da ake yi daga hagu da dama da mu ‘yan sanda ba zai iya dogara da zarge-zarge ba tare da share shi ba.
“Daga baya masu ruwa da tsaki da na tuntuba sun shaida min cewa ba za su iya zuwa wurin Honourable Yakubu ba, don haka na fada musu karara cewa ba na jira su kawo min Yakubu da Bakaro ba, zan fita na kama su. Sai na ce musu kar su ji dadi, daga nan sai na tura jami’ai na su lallaba cikin kowane lungu da sako da wadannan mutanen suke, amma da jin cewa ina neman su, sai suka gudu daga jihar Bauchi.
A wani labarin kuma:Mataimakiyar Gwamnan Kaduna ta ziyarci Zangon Kataf, ta yi Allah wadai da kashe-kashe
Biyo bayan kashe-kashen da aka yi a karamar hukumar Zangon Kataf, mataimakiyar gwamnan jihar Kaduna, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe a ranar Larabar da ta gabata, ta jagoranci tawagar jami’an gwamnati domin jajantawa al’ummar yankin.
Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe, yayin da ta ke yin Allah wadai da kashe-kashen, ta ce sun je ga al’ummar domin isar da ta’aziyyar Gwamna Nasir el-Rufai da daukacin al’ummar jihar ga Agwatyp, HRH Dominic Gambo Yahaya da iyalan wadanda suka rasu.