Majiyar mu ta kawo mana Labarin da ya shafi tattalin arzikin kasa ,Dole kafin Karin albashi ya samu sai gwamnati tayi haka zai tabbata.
A shekarar nan ne dai ko tun kafin ta akayi ta kai ruwa rana Dan samun dai dai to tsakanin Majalisa da bangaren Gwamnati kan 30,000 mafi karancin albahshi a ma’aiktan kasar nan.
Sai dai in har hakan zata kasance dole sai an sake zuba kudi a bangaren hakan na zuwa ne juma’ar da ta gabata saboda rashin isasshen kudin shiga na haraji VAT ta duba domin iya biyan 30,000,sai dai kuma gwamnati ta tsayar da dalar Amurka akan naira 305 a kasuwa.
Sai kuma bangaren rarar man fetur Wanda shima indai za a daina biyan tallafin to shima zaisa a iya biya.
A 17 ga watan mayu albahshi na jami’an tsaro ya karu da biliyan 250 dalilin wannan Kari da aka samu,haka nan masu yiwa kasa hidima Karin zai shafe su.
Naira biliyan 70 zata kara a cikin kudin da take kashewa a kan albahshi idan aka soma biyan masu yiwa kasa hidima ta NYSC wanann sabon na 30,000 a maimakon abin da aka saba basu na 18,000 ko wane wata.