Dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar PDP kuma gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa, ya bayar da tabbacin cewa jam’iyyar za ta shiga zaben badi a matsayin jam’iyya daya, mai membobin dake da hadin kai.
Okowa ya bayyana haka ne a masaukin gwamnan jihar Benue, a Asokoro, Abuja yayin da yake zantawa da manema labarai bayan ganawar sirri da Gwamna Samuel Ortom.
Ya ce tsarin sulhun da shugabannin jam’iyyar suka bullo da shi don warware duk wasu batutuwan da suka taso daga zaben fidda gwani na shugaban kasa da kuma fitowar sa a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa, yana mai jaddada cewa a karshe “dukkan batutuwa za a warware su.”
KASANCE TARE DA DIMOKURAƊIYYA TV A KODA YAUSHE 👇👇👇
Mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ya bayyana cewa gwamnan jihar Ribas, Nyesom Wike mutum ne mai karfin da yake rike da jam’iyya, wanda kuma ya yi aiki tukuru domin samun nasarar jam’iyyar PDP kuma ba zai so ya yi wa wata jam’iyyar siyasa aiki ba.
A nasa jawabin, Gwamna Samuel Ortom ya tabbatar da matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa, inda ya ce shugabannin jam’iyyar PDP na ci gaba da tattaunawa don gyara duk wani abu da ka iya faruwa bayan zaben fidda gwani na shugaban kasa.
Gwamna Ortom ya bayyana cewa a matsayinsa na mai matukar muhimmanci kuma babban mai ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP, Wike na bukatar a sanya shi don tabbatar da cewa sulhun ya kasance cikin sauki da kwanciyar hankali.