El-Rufai ya umurci Ma’aikatun Kaduna da su karbi tsofaffin Kuɗi
Gwamna Nasir el-Rufai na jihar Kaduna ya umurci masu karɓar kuɗaɗen shiga na Ma’aikatu, da Hukumomi, da ke jihar da su karbi tsofaffin takardun kudi na Naira.
Umurnin El-Rufa’i ya dogara ne akan hukuncin da kotun koli ta yanke kan tsofaffin takardun naira.
KARANTA WANNAN LABARIN: Zaben Shugaban Kasa: Ba Zamu Taɓa Haɗa Kai Da PDP – Inji Al-Mustapha
Wata sanarwa da mai baiwa gwamnan shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Muyiwa Adekeye, ya fitar ta ce: “A bisa bin umarnin kotun koli, gwamnatin jihar Kaduna ta umarci ma’aikatunta da sassanta da hukumominta da su tabbatar da cewa jami’an tattara kudaden na su sun ci gaba da karbar kudaden da ake biya a duk nau’o’in naira, tsoho da sabo.
“Masu tattara kudaden da hukumomin gwamnatin jihar suka ba wa ‘yan kasa hanya don biyan kudi, kuma ana sa ran su bi umarnin kotu.”
El-Rufai dai ya yi adawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari kan umarnin da ya bayar na haramta amfani da tsohuwar N500, da kuma N1000 duk da hukuncin kotun koli.
Jigon na APC ya zargi Buhari da barin miyagu su yi amfani da shi wajen yakar jam’iyyar All Progressives Congress, APC.
El-Rufai ya ce mutanen da ke amfani da shugaban kasa a matsayin makamin kayar da jam’iyyar APC na yin haka ne saboda sun kasa tilasta wa nasu dan takarar jam’iyyar a zaben fidda gwani na watan Yuni 2022.
Gwamnan ya mayar da martani ne kan sanarwar da Buhari ya yi kan manufofin sake fasalin kudin Naira da kuma matsalar kudin da ‘yan Najeriya ke fama da su.
Ya kuma jaddada cewa tsohon kudin naira zai kasance a jihar Kaduna.
A wani labarin kuma: Duk Satar Da Ku Ka Yi Yanzu Ba Ta Da Amfani — Kwankwaso Ya Caccaki Gwamnonin Da Ke Sukar Buhari
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Action Alliance don zaben 2023, Manjo Hamza Al-Mustapha (ritaya), ya yi watsi da rahotannin da ke cewa jam’iyyarsa ta amince da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP.
A babban taron yakin neman zaben Atiku da aka gudanar a Adamawa ranar Asabar, shugaban jam’iyyar APM na kasa, Yusuf Dantele, ya ce jam’iyyarsu da wasu mutane hudu sun amince da Atiku.