Arsenal za ta ci gaba da zama ta daya a teburin Premier akalla har zuwa yammacin ranar Lahadi, bayan da ta doke Bournemouth da ci 3-0 a ranar Asabar.
Gunners na ɗaya daga cikin ƙungiyoyi biyu da suka ji daɗin fara sabuwar Kakar bana, yayin da itama Manchester Cityta zama a kan gaba wajen murnar.
Don adawa da shirin Cherries, mutanen Mikel Arteta sun tashi tsaye wajen ganin sunyi nasarar zama akan gaba bisa jagoranci kyaftin dinsu Martin Odegaard.
Odegaard ne ya ci wa Arsenal kwallo ta biyu kafin William Saliba ya farke wa kulob din.
Arsenal yanzu tana da maki tara a wasanni uku na farko a karon farko tun 2005. Duk da haka, City na iya gogawa da ita idan suka ziyarci Newcastle United a yammacin Lahadi.
‘Yan Pep Guardiola sun doke West Ham da Bournemouth a wasanni biyu na farko.