Akalla Yara uku ne a yankin Badarawa, da ke karamar hukumar Kaduna ta Arewa, suka sami mummunan raunika, bayan wani Abu ya fashe.
Jaridar DAILY POST ta ruwaito cewa, lamarin ya afku ne da yammacin yau Asabar, lokacin da yaran su ke tsaka da wasannin su.
Sai dai haryanzu ba’asami cikakken rahotan wadanda suka sami raunukan ba, amma an ruwaito cewa, daya daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da su, ya rasa hannayan shi biyu.
Lokacin da Jaridar DAILY POST ta tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan jihar Kaduna, ASP Mohammed Jalige, ya tabbatar da afkuwar lamarin.
KARANTA WANNA LABARIN: Harsashi ya kashe wata daga cikin masu zanga zanga a Legas
Jami’in ya bayyana wa wakilin jaridar cewa, “Yanzu haka Ina asibiti da aka kai wadanda lamarin ya rutsa da su, domin kula da lafiyar su” inji shi.
A karshe ya kuma ce, ” Rundunar yan sandan jihar ta baza jami’an ta, a inda lamarin ya afku, domin binciken meye musabbabin fashewar”