Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya bada Umarnin sassauta dokar kulle a ranakun Litinin domin al’ummar jihar su ci gaba da yin zirga-zirga.
Hakan ya fito ne daga bakin sakataren yada labarai na gwamnan Mista Abba Anwar a yammacin ranar Lahadi.
“Mai girma gwamna ya bada Umarnin kara ranar Litinin ta zamo daga cikin ranakun da mutane zasu ke fita”.
“Kuma gwamna ya ja hankali mutane da su ci gaba da bin dokokin da aka kafa domin dakile cutar Corona”.
Mutane zasu ke yin zirga-zirgarsu tun daga karfe 6 na safe har zuwa 6 na yamma, gwamnan ya ja kunnen mutane da su tabbatar sun bi dokar da masana suka gindaya.