Sarkin garin Anka a jihar Zamfara, Alhaji Attahiru Ahmed, ya gargadi wadanda suke da karamin karfi kuma samun su na yau da kullum bai taka kara ya karya ba, a kan su guji auren mace fiye da daya. Kamar yadda kamfanin dillancin labaran Nijeriya ya labarto.
Basaraken na Arewa ya yi wannan gargadin ne a ranar Lahadi cikin fadarsa da ke garin Anka, ya ce aurace-auracen da ake kullawa a tsakanin masu karamin karfi shi ne ke ‘kara jefa kasarnan cikin matsi na tattalin arziki da haddasa katutu na talauci.
Ya ci gaba da cewa: shakka babu, masu hangen nesa da dama sun fadakar tare da jan hankali a kan auren mace fiye da daya ga wadanda samun su bai da wani tasiri wajen kula da harkokin iyali da kuma dawainiyar rayuwarsu ta yau da kullum.
Alhaji Attahiru ya bayyana hakan ne a yayin da ya ke rarraba wasu kayayyakin tallafi na dogaro da kai ga Mata wanda uwar gidan gwamnan Zamfara, Hajiya Aisha Bello Matawalle ta bayar ga kananan hukumomin da suke shiyyar Zamfara ta Yamma da suka hadar da Anka, Bukkuyyum, Gummi, Maradun, da Talata-Mafara.
Alhaji Attahiru a wani bangare na bayaninsa, ya ce; ma’aikatan da samun su bai wuce Naira Dubu 15 ba a kowanne wata, auren mace fiye da daya ba na su bane domin ba za su iya daukar nauyin iyalan su ba.
Ya ce; “Wannan lamari shi ke haddasa karuwar rashin samun ilimi musamman a tsakanin yara a sanadiyyar gazawar iyayen su wajen daukar nauyin da rataya a wuyansu. Ya kamata mutane su rinka sara su na duban bakin gatari a yayin aure gwargwadon karfin samun su domin samun damar daukar nauyin ‘ya’yansu ta fuskar ingantaccen ilimi da kuma kyakkyawar dabi’a ta tarbiyyantar da su.”
A yayin da yake yabawa wannan goma ta arziki ta Hajiya Aisha, Sarkin ya kuma shawarci wadanda suka samu tallafi matar gwamnan da su yi tattalin arzikin da suka samu wajen dogaro da kai da kuma kula da iyalansu ta mafificiyar hanyar dace.