An soke gasar kwallon kafa ta kasar Holland ba tare da fayyace kungiyar da ta lashe gasar ba.
Sannan kuma babu kungiyoyi da za su nitse kasa.
Matakin ya biyo bayan hukuncin gwamnati na haramta duk wani gagarumin buki saboda cutar Korona har sai zuwa 1 ga watan Satumba.
Hukumar da ke kula da gasar ta kasar Holland ta ce babu yadda za a yi a kammala gasa a kakar 2019 zuwa 2020.
Kafin a dakatar da gasar kungiyar Ajax ce a saman tebur inda ta dara AZ Alkmaar da yawan maki.
A yanzu Ajax da AZ Alkmaar ne za su buga gasar zakarun Turai a yayin da Feyenoord da PSV za su je gasar Europa