• About Us
  • Blog
  • Gwamnatin Jihar Kano ta ce ana gabda fara ginin masana’antun Iskar Gas a Jihar
  • Home
Tuesday, February 7, 2023
  • Login
Dimokuradiyya
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio
No Result
View All Result
Dimokuradiyya
No Result
View All Result
Home Labarai

Gidauniyyar Hajiya Lami Ta Tallafawa Mutane 200 Da Magani

said by said
August 17, 2020
in Labarai
Reading Time: 3 mins read
0 0
0
0
SHARES
4
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Hajiya Lami foundation da ke garin Samaru a karamar hukumar Sabon Gari a jihar Kaduna sun bayar da tallafi ga mutane a kalla 200.

Cibiyar dai kamar yadda bincike ya nuna,  mahaifiyar Honorabul Yusuf Shaka, dan takarar kujerar karamar hukumar Sabon Gari ne a shekarun da suka gabata ta kafa ta tare da gudummawar yaranta da suke aiki a wurare daban-daban wanda kuma suka yi fice wajen taimako a duk inda suke gida da waje.

Kuma bincike ya tabbatar da cewa gidauniyar an kafa ta ne don taimakawa marasa galihu musamman a bangarori daban-daban na rayuwa ciki harda bangaren kiwon lafiya.

Tuni wannan gidauniyar ta sami yabo mai yawa wajan jama’ar karamar hukumar Sabon Gari bisa yadda suke gudanar da aikinsu na tallafawa al’umma lokaci bayan lokaci.

A wannan lokacin ma gidauniyar ba ta yi kasa a guiwa ba wajen bayar da tallafin kamar yadda ta saba musamman ganin yadda mutane suka galabaita a sanadiyar annobar cutar korona kamar yadda wakilinmu ya ruwaito mana.

Hajiya Lami Foundation ta baiwa mutane 200 tallafin magunguna tare da yi musu  gwaje-gwaje akan matsaloli mabambanta.

Daga cikin matsaloli sun hada da zazzabin cizon sauro da matsalar hawan jini sai ciwon suga da dai sauran cutuka dake addabar jama’a a yanzun Kuma a wannan lokacin.

Gamayyar likitoci ne daga cibiyoyin aikin lafiya a Kaduna da Zariya suka kasance a wajen bayar da tallafin Inda kungiyar (Red cross) suka bayar da kariya ga marasa lafiya da masu aikin lafiyar.

Ganau sun tabbatar da cewa babu wata Gidauniya a fadin jihar Kaduna dake gudanar da aikin taimakon talaka a bangaren kiwon lafiya kamar yadda Gidauniyar Hajiya Lami  ke gudanarwa a wannan lokacin .

Ganau sun kara bayyana cewa, ko yanzu in har mara lafiya na da takardun da suka nuna cewa likitoci suka rubuta mashi musamman ABUTH to duk maganin da aka rubuta mashi mara lafiyar, to Gidauniyar za ta nemo maganin komin tsadarsa su ba mara lafiyar kyauta ba sisin kobo.

Malama Rabi Ibrahim mai fama da ciwon hawan jini na daya daga cikin wadanda suka amfana da tallafin, a yayin da take hira ga manema labarai bayan an yi mata gwaji tuni ta nuna jindadinta tare da yiwa yara da jikokin Hajiya Lami tare da fatan Allah ya biya musu bukatar su duniya da lahira.

Dakta Muhammad na daya daga cikin likitoci da suka duba mutanen da aka gwada, shima ya nuna Jindadinsa bisa yadda aka ba su goyan baya har suka duba mutane 200 ba tare da wani hatsaniya ba, kuma ya yi fatan alheri ga dukkan ‘ya’yan Hajiya Lami da suke bayar da gudummawarsu don taimakawa al’umma.

Alhaji Imran shi ne shugaban shiyya na kungiyar ‘Red cross) a karamar hukumar Sabon Gari a jihar Kaduna kuma shi ya jagoranci kungiyar ta su, shima ya yabawa ayarin likitoci da masu bada maganinsu (pharmacist) da jama’ar garin Samaru baki daya bisa hadin kai da suka bayar yadda aka fara lafiya haka aka gama lafiya. .

Hajiya Lami, Mahaifiyar Honorabul Yusuf Shaka ita ce uwa ga Gidauniyar kuma karkashinta ne gidauniyar take gudanar da aiki a na ta kalaman lokacin da aka kammala bayar da tallafin ga Jama’a ta ce; “Ina godiya ga Allah madaukakin Sarki Kuma na roki Allah ya karawa Annabi daraja tare da Sahabbansa baki daya”.

Ta ci gaba da cewa; “gaskiya bani da abin da zance illah in ce Allah ya yi wa ‘ya’yana albarka don sune suke gudanar da wannan hidimar, ga shi kuma Ni ake godemawa don hakan Allah ya kara tsare su a duk inda suke, su kuma jama’a Allah ya baiwa kowa lafiya na gode kwarai da gaske”.

An yi taro lafiya an tashi lafiya.

Previous Post

Dalilan Da Ya Sanya Kotu Ta Soke Zaben Gwamna Diri Na Jihar Bayelsa

Next Post

Marasa Aikin Yi A Nijeriya Na ‘Kara Hauhawa

Next Post

Marasa Aikin Yi A Nijeriya Na 'Kara Hauhawa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result
Arabic Arabic English English French French Hausa Hausa
  • Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    Ya ce mun shi Dillalin Motoci ne, bayan mun yi aure na gane Makanike ne

    2328 shares
    Share 931 Tweet 582
  • Sai na yi lalata da kai na kwanaki 4 babu ƙaƙƙautawa sannan zan taimaka maka, Wata mata ga saurayi

    1491 shares
    Share 596 Tweet 373
  • CBN Ya Sake Fitar Da Sabbin Bayani Kan Dawo Da Tsofaffin Takardun Kudin Naira

    1401 shares
    Share 560 Tweet 350
  • Rikicin Takara Gwamnan Adamawa A APC: Kotu Ta Tsayar Da Hukunci Kan Nuhu Ribadu Da Yake Yiwa Binani

    1051 shares
    Share 420 Tweet 263
  • Yan sanda a Katsina sun cafke yaro dan shekara 13 saboda ya kashe yan ta’adda

    991 shares
    Share 396 Tweet 248
Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5

Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5

February 7, 2023
‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo

‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo

February 7, 2023
NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

February 7, 2023
Shugaban INEC Ya Gana Da Emefiele Kan Sabbin Manufofin Kudin Naira

Shugaban INEC Ya Gana Da Emefiele Kan Sabbin Manufofin Kudin Naira

February 7, 2023
Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan Ya Yi Babban Rashi

Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan Ya Yi Babban Rashi

February 7, 2023
Rashin Tsaro: Shugaban INEC Ya Gana da NSA Gabanin Zaben 2023

Rashin Tsaro: Shugaban INEC Ya Gana da NSA Gabanin Zaben 2023

February 7, 2023
Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5
Siyasa

Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5

February 7, 2023
‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo
Labarai

‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo

February 7, 2023
NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023
Labarai

NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

February 7, 2023
Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5

Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5

February 7, 2023
‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo

‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo

February 7, 2023
NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

February 7, 2023

Twitter

Archives

Recent Posts

  • Ka Yiwa Allah Ka Shiga Tawagar Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Na PDP – Iyorchia Ayu Ya Roki Gwamnan G5
  • ‘Yan Najeriya Zasu Yiwa Shugabanni Hisabi a Lokacin Zaben 2023 — Osinbajo
  • NSA Ya Yiwa Shugaban INEC Alkawarin Samar Da Cikakken Tsaro a Lokacin Zaben 2023

Quick Links

  • Tsaro
  • Siyasa
  • Labarai
  • Wasanni
  • Kasuwanci
  • Rikicin Duniya

Contact Us

info@dimokuradiyya.com.ng

0809 912 4425 +234 809 912 4425

No. 218 Mogadishu layout Kaduna City Center Ahmadu Bello way kaduna. Kaduna, Nigeria 800273

Copyright © 2022 Dimokuradiyya Media Services LTD.

No Result
View All Result
  • Home
  • Labarai
  • Siyasa
  • Rahotanni
  • Wasanni
  • Rikicin Duniya
  • Nishadi
  • More
    • Kasashen Ketare
    • Kiwon Lafiya
    • Ilimi
    • Kasuwanci
    • Noma Da Kiwo
    • Labarun Mako
    • Talla
    • Masarautu
    • Babu Maraya
    • Addini
      • Wa’azin Kirista
    • Girke-Girke
    • Waiwaye
    • Marubutanmu
    • Wasiku
    • Ni’ima Dai Mata
    • Tsaro
    • Bidiyo
    • Audio

Copyright © 2022 Dimokuradiyya Media Services LTD.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In