Hukumar Bayar Da Agajin Gaggawa Ta Kasa Da Kasa Ta Red Cross Reshen Jihar Kano Ta Shirya Wani Taron Karawa Juna Sani Tsakanin Jami’an Ta Da Kuma Hukumomin Dake Da jibi da Bayar Da Agajin Gaggawa A Mataki Na Farko da nufin duba kan ma’aikatan lafiya dake fuskantar hadari a yayin byar da wannan taimakon.
Taron dai ya kasance na wuni daya inda aka tattauna kan matsaloli da dama da ma’aikatan lafiya suke fuskanta musamman yayin gudanar da ayyukan su, kazalika a wajen kuma an bayar da hanyoyin mafita da dama wadanda zasu taimaka wajen kawar da wannan matsalar ga jami’an lafiya.
Taron wanda ya samu halartar wasu daga cikin manema labarai anan Kano da kuma hukumomin tsaro das ka hadar da rundunar sojin kasa, rundunar yansanda, rundunar tsaro ta civil defence, hukumar Karota, da kuma wakilin hukumar tsaro ta DSS da sauran su, ya gudana ne anan Kano a unguwar nasarawa GRA.
Kazalika an mayar da hankali ga irin gudnmawar da wasu bangarori zasu bayar domin magance matsalar.
Daga cikin bangarorin sun hadar da bangaren gwamnati a mataki na jihar, bangaren al’ummar gari, da kuma kungiyoyi masu zaman kansu.
Babban sakataren kungiyar ta RED CROSS a Kano Alhaji Musa D Abdullahi yayi Karin haske kan makasudin shirya taron.
”Mun shirya wannan taron ne sakamakon yadda ma’aikatan lafiya ke cigaba da fuskantar matsala, musamman wajen kai marasa lafiya asibiti, mun kuma kalli yadda ake amfani da jiniya ba bisa ka’ida ba wanda itama matsala ce ta daban.” inji shi.
A yayin taron an bayyana cewa babban matakin da gwamnati zata bayar wajen kare jami’an lafiya masu bayar da agajin gaggawa ko kuma kawar da barazanar da suke fuskanta ya hadar da basu goyon baya dari bisa dari yayin gudanar da ayyukan su. Taimaka musu da kudin alawus alawus akan lokaci da kuma samar musu da kayan aiki na zamani.
Yayin da a bangaren kungiyoyi masu zaman kansu da dama cikin mahalarta taron sun bayyana cewa akwai bukatar kungiyoyi masu zaman kansu su shiga a dama da su wajen tallafawa jami’an lafiyar ta hanyar da ta kamata da kuma taimaka wajen wayar da kan al’umma irin muhimmancin da jami’an ke da su.
Al’ummar gari suma a yayin taron an bayyana cewa suna da rawar takawa wajen magance matsalar ta hanyar bayar da wani abu na su ga jami’an da kuma kare dukiyar wanda ya gamu da iftila’I daga sauran bata gari da dai sauran su.