Tsohon gwamnan jihar Zamfara Abdul’aziz Yari Abubakar ya ce an sha yin sasanci da ‘yan fashi amma hakan bai kawo karshen kashe-kashe ba.
Zamfara na daya daga cikin jihohin da suka fi fama da kalubalen tsaro a arewacin Najeriya, musamman matsalolin hare-haren ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane da kuma barayin shanu.
Kuma sabuwar gwamnatin PDP ta Bello Mutawalle ta ce ta fara bin hanyoyin kawo karshen zubar da jinin da aka shafe shekaru ana kokarin magancewa, ta hanyar sulhu da wadanda take ganin sun jefa jihar halin da ta tsinci kanta a ciki.
Amma tsohon gwamnan jihar Abdul’aziz Yari wanda ake zargin al’amurran tsaro sun tabarbare a Zamfara a zamanin mulkinsa, ya ce ba za a taba sasantawa da ‘yan bindiga ba, ba tare da nuna fin karfi ba.
“Sasanci, na yi na daya na yi na biyu kuma amma na uku na ce ba zan sake ba saboda hakan bai hana abin da ake a Zamfara ba na satar mutane da kasa-kashen mutane da dabbobin jama’a.”
“Dole idan za ka yi sasanci sai an fito a fuskar fin karfi, cewa na fi ka karfi dole ka mika wuya,” in ji Yari.