Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, ya bukaci al’ummar Musulmai a fadin Nijeriya da su yi amfani da watan Ramadan mai albarka wajen yin addu’a wa kasar Nijeriya domin samun zaman lafiya mai daurewa da hadewar kai wuri guda domin ci gaba. A sakonsa na watan Ramadan, Gwamna Obaseki ya shaida cewa, “Al’ummar musulmai a jihar nan da sauran sassan duniya za su fara gudanar da Azumin watan Ramadana, ina amfani da wannan damar wajen jawo hankalinku da ku yi amfani da wannan damar wajen hada kan jama’a da jawo kowa a jika domin daurewar zaman lafiya da ci gaban kasa. “Wata ce mai falala daga Allah wacce musulmai suke gudanar da Ibadarsu a cikinta don haka da bukatar a wannan wata mai alfarma musulmai su shagala wajen yin addu’a zaman lafiya, hadin kai da kuma addu’ar neman ci gaba wa Nijeriya,” Inji gwamnan. Gwamna Godwin ya kuma bukaci al’ummar Musulmai a jihar Edo da cewar su yi addu’a wajen samun ci gaba ga jihar ya nemesu su roki Allah ya bayar da dama wajen ci gaba da gina jihar da daura jihar zuwa matakin da ya dace. Ya yi fatan yadda aka fara lafiya a karasa Azumin watan Ramadana lafiya.