By Abbas Yakubu Yaura
Gwamna Aminu Masari na jihar Katsina yace dole ne a fatattaki ‘yan fashi da makami baki daya a fadin jihohin Arewa da abin ya shafa kafin wa’adin su ya kare a shekarar 2023.
Gwamnan, wanda ya bayyana hakan a lokacin da yake rattaba hannu a kan kudirin kasafin kudin jihar na shekarar 2022 a ranar Laraba a Katsina, yace babu gudu babu ja da baya a yakin da ake yaki da ‘yan bindiga.
Kasafin kudin na naira biliyan 323.3 da aka sanya wa hannu ya yi kasa da Naira biliyan 341 da aka mika wa majalisar dokokin jihar Katsina.
Masari yace, “Dole ne mu shirya mu yaki daidaikun mutane domin yakar ‘yan bindigar domin su miyagu ne kuma suna wakiltar mugaye. Bai kamata mu ja da baya a wannan yaƙin ba.
“Mun karbi ragamar mulkin kasar ne a cikin tsananin barazanar tsaro a shekarar 2015 kuma da yardar Allah, ba za mu mika kasar nan ga al’umma masu zuwa a karkashin wannan yanayi ba. Dole ne mu dawo da al’ada.
“Hanya daya tilo da za mu kalubalanci wadannan mutane ita ce mu nuna musu cewa a shirye muke, da zama da kuma iya kare yankinmu da rayuka da dukiyoyinmu.”
Tun da farko, shugaban majalisar Alhaji Tasi’u Maigari ya ce ‘yan majalisar sun samu bayanai daga kungiyoyin farar hula da ‘yan majalisarsu da sauran jama’a kafin su zartar da kasafin kudin.