Gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari ya aike da rubutacciyar hukumar sadarwa ta Kasa NCC wasika inda ya bukaci ta maido da layukan waya a kananan hukumomi goma daga cikin 17 da aka dakarwa kimanin watanni hudu da suka gabata.
Dimokuradiyya ta ruwaito cewa kananan hukumomi goma da abun ya shafa sun hada da Kurfi, Dutsinma, Matazu, Musawa, Malumfashi, Dandume, Bakori, Funtua, Kafur da kuma Danja.
Wadanda shirin maido da aiyukan bai shafa ba sun hada da Faskari, Sabuwa, Batsari, Safana, Kankara, Danmusa da Jibia.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban daraktan yada labaran gwamnan, Abdu Labaran Malumfashi ya fitar a ranar Alhamis.
Idan dai za a iya tunawa gwamnatin jihar Katsina ta zartar da dokar hana aikata laifuka, wanda baya ga dakatar da ayyukan wayar da kan jama’a a kananan hukumomi 17, ta kuma haramta amfani da wasu hanyoyi a yankunan da abun ya shafa, da safarar itace a cikin jihar, da sayar da nau’o’in dabbobi a ciki, da kuma rufe wasu manyan kasuwanni a wuraren da abun ya shafa da kuma sayar da babura a kasuwannin da abun ya shafa da kuma hana amfani da babura da kekunan kasuwanci daga karfe 10:00 na dare zuwa karfe 5:30 na safe a fadin jihar. da sauransu.
”Hukuncin da gwamnati ta yanke na dakatar da a dokar a kananan hukumomi goma ya biyo bayan dawowar al’amuran yau da kullum, duk da cewa ana cigaba da kokarin ganin an samu zaman lafiya a kowane bangare na jihar”. ‘ in ji sanarwar.