Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa ta kammala duk wani shirye-shirye da ake bukata domin dawo da tsarin iyakar shiga cikin Gari a manyan hanyoyin da ke cikin fadin Nijeriya.
Wannan bayanin na zuwa ne bayan Ministan ayyuka da gidaje Babatunde Fashola ya tabbatar da cewa za a dawo da wannan tsari kwanan nan. A Ranar Laraba 2 ga Oktoba, Fashola ya ce sun gama wannan shirin.
Bayan kammala taron majalisar zartarwa na wannan makon, Mista Babatunde Raji Fashola ya fadawa ‘yan jarida cewa babu wani dalili na daina tare Matafiya a kan manyan titunan kasar.
Ministan kasar ya ci gaba da cewa: “Babu dokar da ta ce a cire shingen kan hanyoyin da ke Nijeriya. Mu na sa rai mu dawo da karbar kudi a kan tituna; mun kammala zanen gine-ginen.”
Fashola ya ce yanzu an kammala aiki kan irin ginin da za a yi, da kuma kayan da za a yi amfani da su da yadda aikin zai kasance. Abin da ya rage shi ne abubuwan da za a yi la’akari da su.
Ministan ayyukan ya nuna cewa su na kokarin ganin yadda za a yi watsi da batun karbar kudi a kan hanyoyin tare da ganin ba a batawa mutane lokaci a sakamakon binciken da za a rika yi.
“Mu na kuma bukatar karin fili domin a gina shinge mai layi 10. Abin da wasu ke tunani shi ne da kudin da aka tara a kan titunan za a rika gyara hanyoyin.” In ji shi.