By Abbas Yakubu Yaura
A ranar Laraba ne hukumomin jihar Borno da sojoji suka bude hanyar Bama zuwa Banki da kuma zuwa kasar Kamaru mai nisan kilomita 65, wanda aka rufe tun a shekarar 2012 daba a samu damar shige da fice, sakamakon hare-haren ‘yan tawaye a yankin, Hanyar dai ta hada kasar Kamaru da wasu sassan Afirka ta tsakiya.
Gwamna Babagana Zulum, tare da Kwamandan, ‘Operation Hadin Kai’, Manjo Janar Musa Christopher, sun sake bude hanyar a mahadar Banki dake wajen garin Bama.
Wata sanarwa da mai baiwa gwamnan shawara na musamman kan hulda da jama’a da dabaru Malam Isa Gusau ya fitar, tace jihar ta baiwa rundunar motocin aiki guda 10 domin ci gaba da sanya ido a yankin.
Sanarwar tace gwamnan ya yaba da kokarin shugaban kasa Muhammadu Buhari kan nasarorin da ake samu na yaki da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas.Sanarwar ta kara da cewa gwamnan ya kuma gargadi jami’an kan iyakokin kasar kan karbar kudi tare da bayar da umarnin kama duk wanda ke da hannu wajen safarar kayayyaki a kan hanyar.
Tun da farko, kwamandan ya godewa gwamna Zulum bisa goyon bayan da yake baiwa sojoji a yakin da suke yi da ‘yan tada kayar baya, ya kuma ce sake bude hanyoyi da sake tsugunar da ‘yan gudun hijirar na nuni da kawo karshen ta’addancin.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa gwamnan ya kai ziyarar bazata zuwa Kwalejin Ilimi ta Umar Ibn Ibrahim (UICEST) Bama, inda ya umurci kwamishinan da a sake ginawa da sake tsugunar da jama’a (RRR), sannan ya bukaci Mustapha Gubio, daya gaggauta samar da motocin bas ga daliban.