Gwamnan Ondo da shugaban hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi NDLEA, sun shilla zuwa kasar Thailand Dan sanin yadda ake shuka Ganyen Tabar Wiwi.
Gwamna Rotimi Akeredolu, tare da shugaban hukumar Muhammad Mustapha Abdallah.
Gwamnan ya bayyana haka ne 14 ga watan mayu inda yace sunje samo wani ilimi ne Dan kara samun hanyoyin kudin shiga na jahar da kuma amfani da shi ta hanyar da ya dace.
Ya kara da cewa tawagar tasu zata karanci dabarun noman tabar ta wiwi Dan yin magunguna tunda ondo itace jaha daya tilo mai Samar da wiwi inda zata Samar da dala biliyan 145 a kasuwar hada wiwi a shekarar 2025.
Ba karamar asara zamu tafka ba in bamu shiga wannan harka ba a cewar Gwamnan.
Zamu karkata hankulan mu wajen yin magani da ita karkashim sa’idon hukumar ta NDLEA shi yasa ma na gayyaci shugaban Dan ya shaida kuma a san ta yadda zamu shiga harkar Gadan Gadan.
In ba a manta ba NDLEA ta kama mutane 9,824 a 2018 kan ta ammali da miyagun kwayoyi.