By Abbas Yakubu Yaura
A ci gaba da kokarin samar da yanayi mai kyau na ilmantarwa a fannin kiwon lafiya, gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya amince da siyan janareta KVA 159,da biyan alawus alawus ga dalibai 70 na ungozoma, da gina gidaje 15 a kwalejin koyon aikin jinya da ungozoma ta Shehu Sule dake Damaturu.
Buni ya bayyana haka ne a ranar Talata a wajen bikin yaye ma’aikatan jinyar ungozoma 248 a hukumance a kwalejin jinya ta Damaturu.Gwamna Buni ya bayyana cewa gwamnatin sa na baiwa fannin lafiya da ilimi muhimmanci da dai sauransu.
Sannan yace kwalejin ta kasance daga cikin sassan biyu don haka ana ganin tana da matukar muhimmanci ga gwamnati wajen samar da kwararrun ma’aikatan kiwon lafiya da ake bukata domin yi wa jama’a hidima.
“Bukatar samun isassun ma’aikata da kwararrun ma’aikata domin wannan gwamnati ta yi nasara a yunkurinta na inganta harkokin kiwon lafiya a jihar ba za a iya karewa ba.Wannan ya bayyana dalilin daya sa gwamnati ta kashe kudade da yawa wajen horar da wadannan ma’aikatan jinya da ungozoma da muke bikin yaye su a jihar.a wannan lokaci.
“Ina mika sakon taya murna ga daukacin dalivan da za a ba su satifiket a yau domin samun nasarar kammala karatun su. Lallai kun sanya gwamnati da iyayenku alfahari. Ina rokon ku da ku kasance jakadu na kwarai na Kwalejin da yin hidima ga jama’a cikin mutunci.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa “Tuni gwamnati ta baiwa mutane 231 aiki daga cikin 248 da suka yaye.sannan an umurce ku daku ci gaba da jajircewa kan ayyukanku. Ya kamata ku kasance masu bin ka’idodin sana’ar ku don samar da ayyuka masu inganci don tabbatar da saka hannun jarin gwamnati na horar da ku.
“Haka zalika abin farin ciki ne yadda muka cika alkawarin da muka dauka na gina dakunan kwana na ‘yan mata mai gadaje 200, da gina titi mai nisan kilomita 1.5 da magudanar ruwa mai nisan kilomita 3.0 a cikin Kwalejin domin samar da yanayi mai kyau na bunkasa ilimi,” inji shi.
Da yake jawabi, kwamishinan lafiya na jihar yobe, Dakta Mohammed Lawan Gana, yace an kafa kwalejin ne a shekarar 1993, inda ya jaddada cewa sama da dalibai 20 ne suka yaye da matsakaicin kashi 90 bisa dari 100 .