Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantun gaba da sakandire JAMB, ta ce tana duba yiwuwar fara bayar da gurbin karatu ga ɗalibai a wannan shekara.
Wannan na cikin wata sanarwar da hukumar ta fitar mai ɗauke da sa hannun mai magana da yawun hukumar Fabian Benjamin.
A cewar sanarwar, hukumar ta JAMB za ta gana da shugabannin Jami’o’in ƙasar nan, da nufin dubu tsare-tsaren da hukumar da za ta fitar don fara bai wa ɗaliban gurbin karatu a Jami’o’in faɗin ƙasar nan.
https://dimokuradiyya.com.ng/jamb-za-ta-bada-gurbin-shiga-jamia-na-2020/
Ta ce, za a gudanar da tattaunawar ne kan bayar da gurbin karatu da kuma dabarun daƙile cutar corona, a tsakanin ɗalibai da suka rubuta jarabawar
A cewar hukumar, za ta kuma duba yiwuwar bai wa duk ɗaliban da suka rubuta jarabawar JAMB gurbin karatu a Jami’o’in ƙasar nan, da nufin basu ƙwarin gwiwa ta fannin neman ilimi.