By Abbas Yakubu Yaura
Rundunar tsaro ta farin kaya ta jihar Ondo tace ta cafke wasu mutane 8 da ake zargi da yin safarar haramtattun man iskar gas da aka fi sani da dizal a yankin Abereke dake karamar hukumar Ilaje a jihar.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Hukumar NSCDC ta kuma damke gurbatattun man fetur lita 39,200 da aka kama daga hannun wadanda ake zargin.
Da yake gabatar da wadanda ake zargin a ranar Talata, Kwamandan NSCDC na jihar Ondo, Mista Hammed Abodunrin, yace an kama wadanda ake zargin ne biyo bayan wani rahoton sirri da aka baiwa hukumar.
Yace, “Bisa la’akari da sahihan bayanan da rundunarmu ta samu ta samu wasu dillalan man fetur ba bisa ka’ida ba kuma suka shiga aikin sanya ido a magudanar ruwa na kimanin makonni biyu. Duk da haka, rashin sa’a ya kare daga gare su yayin da aka gansu aka kuma kama su a yankin Abereke.”
A cewarsa, a yayin da ake binciken wadanda ake zargin da suka shigar da kara wajen aikata laifin sun sanar da hukumar cewa sun yi lodin jiragen ruwan ne wanda suka taso daga jihar Delta.
“Sun yi ikirarin cewa wani Mista Adeyemi Ogunkade ne ya basu kwangilar wanda ya mika musu kwale-kwale da man dizal. Na farko, na biyu, da na uku anyi lodin ne da ganguna 40 mai cin lita 200 kowanne yayin da jirgin na hudu ya kai ganguna 36 na lita 200 kowanne wanda adadinsu ya kai lita 39,200 na man da ake zargin gurbatattun man iskar gas ne,” a cewar Abodunrin.
Shugaban NSCDC ya jaddada cewa rundunar dake karkashin ikonsa zata ci gaba da yaki da matsalar barna da kuma mu’amala da man fetur ba bisa ka’ida ba.sannan ya kara da cewa za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike kan lamarin.