Daga: Abbas Yakubu Yaura
Cocin Katolika ta yi kira ga gwamnan jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, da ya dakatar da aiwatar da ka’idojin daukar ciki a jihar.
Kwanan nan ne jihar ta fitar da wata takarda mai shafi 40 mai taken ‘Ka’idojin jihar Legas kan amintaccen dakatar da daukar ciki don dalilai na shari’a.
KARANTA WANNAN LABARIN: https://dimokuradiyya.com.ng/yan-sanda-sun-kama-jamian-bankin-da-ke-shirya-makarkashiyar-yin-fashi/
Sai dai cocin ta ce hujjar da ma’aikatar lafiya ta jihar Legas ta bayar na bayar da ka’idojin ba komai ba ne illa wata hanya ta halasta zubar da ciki ta bayan gida.
Cocin ta ce ba wai kawai rashin gaskiya ba ne, har ma ba za a amince da ita ba, ta kara da cewa ka’idojin ba komai ba ne illa hanyoyin samar da dakin zubar da ciki ba gaira ba bu dalili.
Da yake watsi da ka’idojin, Babban Bishop na Katolika na Legas, Most Rev. Adewale Martins, ya ce ba gaskiya ba ne cewa an tuntubi duk masu ruwa da tsaki a cikin shirye-shiryen jagororin.
Daraktan Sadarwa na Zamantakewa, Archdiocese Legas, Rev. Fr. Anthony Godonu, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi.
Sanarwar ta ambato Martins na cewa, “Cocin Katolika da duk masu kishin da’a suna adawa da duk wani nau’in hanyoyin zubar da ciki wanda manufarsa kai tsaye ita ce ta kawo karshen rayuwar jariri a cikin mahaifa.
“Yaron da ke cikin ciki yana da hakkin ya rayu kuma a kiyaye shi kuma kada a kashe shi ta hanyar rashin adalci.
“Mun yi imani da gaske cewa dole ne a mutunta kowane ran dan Adam da kuma kiyaye shi musamman wadanda suka fi rauni a cikin mahaifa tun daga lokacin da suka dauki ciki.
“Babu wani abu kamar yaron da ba a so domin kowane yaro baiwa ce daga Allah da ya kamata a rene ta kuma a bar ta su girma domin cika manufarsu ta rayuwa.
“Muna bukatar mu ci gaba da lalubo hanyoyin bayar da tallafi ga matan da suka samu kansu cikin wahalhalu sakamakon daukar ciki maimakon tunanin zubar da yaron da ba shi da wani laifi a cikin wahalhalun da uwa ke ciki.
“Duk wani yunƙuri na kashe rayuwar ɗan da ba a haifa ba, daidai yake da kisan kai kuma ya kamata a ɗauke shi a matsayin babban laifi.
Don haka, ya kamata mu mayar da hankali kan wayar da kan jama’a game da jima’i da hadin gwiwa domin tallafa wa matan da suke da juna biyu ba tare da sun shirya yin ciki ba.”
Ya yi mamakin dalilin da ya sa gwamnatin jihar Legas ta nuna damuwa kan halasta zubar da ciki a daidai lokacin da hatta Amurka da sauran kasashen da suka ci gaba ke bitar matsayinsu kan halasta zubar da ciki kamar yadda aka gani a hukuncin da kotun kolin Amurka ta yanke a baya-bayan nan kan batun zubar da ciki a al’amarin.