By Abbas Yakubu Yaura
Kungiyar Yan jarida reshen Babban Birnin Tarayya Abuja ta nemi afuwar gwamnan jihar Katsina, Aminu Masari bisa zarginsa da kama wani dan jarida da ke Abuja, Nelson Omonu tare da tsare shi.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a daren jiya, majalisar ta ce an yaudari wanda ke da alhakin kama Omonu kamar yadda aka yi masa a gidansa da ke Abuja ranar Asabar.
“Rikicin ya samo asali ne daga bayanan da ‘yan uwa suka bayar, don haka ba manufar kungiyar NUJ ta babban birnin tarayyar Abuja ba ce ta kunyata gwamna da gwamnatin jihar Katsina.
Muna rokon gafarar Gwamna Masari da gaske kuma muna rokonsa da ya amince da hakan a matsayin daya daga cikin gazawar kokarin dan Adam,” wata sanarwa mai dauke da sa hannun Emmanuel Ogbeche da Ochiaka Ugwu, shugaba da sakataren majalisar.
Sai dai kuma Majalisar ta yi kira da a gaggauta sakin dan jaridar.