Ministan Sufurin Jiragen Sama, Sanata Hadi Sirika, ya ce ana sa ran jirgin saman kasar nan wato, Nigeria Air, zai fara aiki nan da Afrilu 2022.
Ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin da yake zantawa da manema labarai na fadar shugaban kasa bayan taron majalisar zartarwa ta tarayya da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta a fadar shugaban kasa dake Abuja.
A cewarsa, kamfanin dakon kaya na kasa zai kasance ne da wani kamfani wanda gwamnatin Najeriya za ta rike hannun jarin kashi 5%, ‘yan kasuwan Najeriya na da kashi 46%, yayin da sauran kashi 49% za a kebe su ne domin har yanzu ba a basu abokan huldar kasuwanci ba, ciki har da kasashen waje masu zuba jari.
Ya ce idan ya fara aiki, kamfanin na kasa zai samar da ayyuka kusan 70,000 ga ‘yan Najeriya