A daren jiya Asabar ne ‘yan bindaga dauke da muggan makamai suka shiga garuruwan sabon Garin Dunburawa ta karamar hukumar Batsari da sabon garin Gamji a karamar hukumar Safana duk a jihar Katsina jim kadan bayan gama sallar Asham.
‘Yan bindagan suka shiga garuruwan inda suka rinka harbin kan mai uwa da wabi.
Har zuwa daidai lokacin da muke hada wannan rahoton bamu samu labarin asarar rayuka ba, anma majiyar mu ta tabbatar mana da cewa an kawo wadanda aka jikkata a babbar asibitin Batsari.
Karamar hukumar Batsari tana daga cikin kananan hukumomin dake fama da tashe-tashen hankula sanadiyyar hare-harem ‘yan bindiga.
Jihar Katsina dai ita ce mahaifar shugaban Najeriya Muhammadu Buhari.