Karancin Naira: Kai Jarumi ne nq wannan lokacin – FFK ya yabawa El-Rufai kan caccakar Buhari
Jigo a jam’iyyar APC, Femi Fani-Kayode ya yaba wa gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai kan matakin da ya dauka kan manufofin babban bankin Najeriya, wato Naira.
DAILY POST ta tuna cewa bayan sake fasalin takardar kudin Naira, babban bankin Najeriya, CBN ya sanya ranar 10 ga watan Fabrairu a matsayin wa’adin ci gaba da yaduwa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Karancin Kudi: Buhari Ya Yi Amfani Da Gurguwar Shawara, Bayan Umarnin Kotun Koli — Keyamo
Sai dai wasu gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar APC, sun maka gwamnatin tarayya zuwa kotun koli a wani mataki na dakatar da aiwatar da wa’adin da aka kayyade.
Da take mayar da martani kan karar da gwamnatocin jihohin Kaduna, Kogi da Zamfara suka shigar a ranar 8 ga watan Fabrairu, kotun koli ta dakatar da babban bankin CBN daga aiwatar da dokar haramta tsofaffin takardun kudi har sai an saurari karar da kuma yanke hukunci a ranar Laraba 15 ga watan Fabrairu.
Da yake jawabi a wani shiri na kasa a ranar Alhamis, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umurci bankin CBN da ya saki tsohuwar takardar N200 yayin da tsofaffin takardun N500 da N1,000 suka daina aiki.
Sai dai El-Rufai a wani jawabi da ya yi a fadin jihar, ya caccaki shugaban kasar, yana mai cewa tsohon N500 da N1,000 na ci gaba da zama a jihar sa, yana mai gargadin cewa umarnin Buhari ya sabawa umarnin kotun koli.
Ya zargi shugaban kasar da kokarin yi wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu zagon kasa.
Da yake mayar da martani, FFK, tsohon ministan sufurin jiragen sama ya bayyana gwamnan a matsayin gwarzon lokacin.
A wasu jerin sakonnin da ya wallafa a shafinsa na twitter, FFK wanda a halin yanzu ake yi masa tambayoyi a ma’aikatar tsaro ta farin kaya, DSS, kan wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter mai cike da cece-kuce, ya ce Tinubu ne zai lashe zaben duk da zargin kulla masa makirci.
Ya rubuta, “Jarumin wannan lokacin shine @elrufai. Ya fadi gaskiya kuma @fkeyamo ya tabbatar da waccan gaskiyar cikin balaga da jajircewa a shirin ‘Siyasa A Yau’ na Channels TV a daren jiya.
“Wadanda suka kitsa tare da kulla makarkashiyar dakatar da BAT da yunkurin cinnawa al’ummarmu wuta da lalata dimokaradiyyar mu sun gaza.
“A ranar Asabar mai zuwa za a kawo karshen wannan lamari, fatan masu kulla makarkashiya za su ruguje, kuma ba wai kawai a wulakanta makiyanmu da cin galaba a kansu ba, har ma a killace su a cikin kwandon shara.
A wani labarin kuma: APC Ta Fara Siyar da Fom Din Tsayawa Takarar Gwamnan Bayelsa, Kogi, Da Imo
Jam’iyyar APC mai mulki ta fara sayar da fom din tsayawa takara a zaben gwamnonin Bayelsa, Kogi da kuma Imo da za a yi a ranar 11 ga watan Nuwamba. Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
Wakilin Majiyar Dimokuradiyya ya ruwaito cewa tuni masu neman takara suka fara karbar fom dinsu a sakatariyar jam’iyyar APC ta kasa da ke Abuja kan kudi Naira miliyan 50.