kuci gaba da kokari har 29 ga Watan mayu.
Daga Abba Anwar.
A zaman ta na karshe majalisar zartarwa ta kano karkashin jagoran cin Gwaman kano dakta Abdullahi Umar ganduje na zangon mulkin sa na farko yazo karshe.
Inda ya yabawa kwamishinonin kan aiki tukuru da kuma yin komai a bude a duk ma’aikatun su a tsawon shekaru Hudu da suka ga bata.
Yayi wananna bayani ne yau laraba yayin da yake Jan ragamar zaman majalisar na karshe a zangon mulkin farko.
“Na gode muku da yadda kuka tafiyar da ma’aikatun Kuma kun zama shugaban ni abun koyi”, inji gwamna ganduje.
Ganduje ya kara gode musu inda yace yadda basu shiga duk wani abin da bai dace ba a zaman Ku a ma’aikatun Ku. Ba Wanda aka taba kamawa da rashawa cikin Ku wanann abun yabawa ne
Ya lissafo abubuwa Wanda har zuwa 29 ga mayun nan na 2019 Inda ya bayyana yau ce ranar karshe ta zaman majalisa amma bawai karshen zangon Ku a ofis ba Ku ci gaba har zuwa 29 ga 2019.
Da yake magana kan mataimakin sa Dakta Nasiru Yusuf Gawuna inda yace yazo ana tsaka da mulki amma ya bada gudunmuwa sosai kan cigaban jaha.
Bayan nan ya juya bangaren sakataren Gwamnatin jaha Alhaji Usman Alhaji inda yace shine mai kula da komai na wannan Gwamnatin.
Da yake magana kan shugaban ma’aiktan jaha Muhammad Awwala na’iya ya ce yayi kwazo matuka tsakanin shi da ma’aiktan jaha tsohon shekaru hudu .yace ya kara dangantaka da gwamnati da ma’aikata.
Na Dade cikin gwamnati shekaru da yawa amma ban taba ganin wacce tayi kwazo da jajircewa a shekaru Hudu da hadin kan ma’aiktan jaha kuma akayi zaman lafiya kamar wannan Ba, inji shi.
Kan Nada sakatere na din din din gwamnan yace munbi matakai da kuma nazari kan kasuwanci kan ya dawo dai dai.
Da yake fayyacewa kan dai nadin sakaterorin yace Gwamnatin tana la’akari da wadanda suka kware kafin a basu dama shiga cikin wanann gwamnati.
Gwamna ya tabbatar wa wadanda suka cike Neman Mukamai bayan an saki sunayen su za a Musu gwaji sannan a basu matsayi.kuma zasu dau tsawon wata Shida kafin tabbatar da su a karshe.
“Sannan dole akwai alamu duk mutanen sai an duba basu da alaka da rashawa kafin basu.
Ganduje ya gode wa duk kwamishinonin yayi zaben gwamna da yagabata,yace ina alfahri da Ku duka kuma muna tare har yanzu ina fatan zaku sauke nauyin aka baku a next level in an baku.
Alhaji Usman sakataren gwamnati yayi magana a madadin su duka inda suka godewa Gwamna da damar da ya basu .
Anwar shine shugaban yada labarai na gidan gwamanti.