A yayin da talakawa ke kukan babu kudi a kasa, kudi yayi karanci a tsakanin jama’a, su kuwa shuwagabannin Najeriya ko a jikin su, sakamakon suna kula da baitul malin gwamnati, don haka suke facaka da kudi son ran su.
Anan gwamnatin jihar Ondo ce ta ware wa ofishin gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu naira miliyan goma sha uku (N13,000,000) don sanya katin kiran waya a kasafin kudin shekarar 2019, kamar yadda majiyar Hausa7 ta ruwaito.
Haka zalika an kasafta kudi naira miliyan dari biyar (N500,000,000) don tarbar manyan baki da ake sa ran za su halarci wasu muhimman bukukuwa ko taruka da gwamnatin jihar za ta dauki nauyi a cikin shekarar 2019.
Sai dai shima mataimakin gwamnan ba’a barshi a baya ba, inda aka ware naira miliyan biyar don sa katin waya a ofishin sa, sai kuma naira miliyan biyu da aka kasafta don sa katin waya a ofisoshin manyan hadiman gwamnan.
Bugu da kari gwamnatin ta kasafta naira miliyan dari uku da talatin da shida don sayan kayan tsaraba da kyaututtuka da za ta raba a yayin bukukuwan kananan yara da kuma naira miliyan dari biyu da talatin don sallama, shi ma ofishin mataimakin gwamna an ware masa naira miliyan hamsin don bayar da kyauta.
Wannan wadaka bai tsaya nan ba, inda aka kasafta wasu kudaden don amfanin ofishin gwamna, inda aka ware naira miliyan dari da bakwai don tafiye-tafiyen cikin gida, naira miliyan biyu kudin wutar lantarki, da kuma miliyan 25 don sayen kayan aiki a Ofis da kwamfutoci.
Duk a cikin wannan kasafin kudi na bana wanda tuni majalisar dokokin jihar ta amince da shi, an ware miliyan 53 don gyaran motoci, miliyan 150 don ciye-ciye da shaye-shaye da dai sauran su.