By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnatin jihar Legas ta ce kusan kashi 89 cikin 100 na makarantun jihar sun bi umarnin komawa aiki ranar 4 ga watan Janairu, 2022.
Darakta-Janar, ta ofishin tabbatar da ingancin ilimi, Misis Abiola Seriki-Ayeni, ta bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Litinin.
Ta ce, “640 daga cikin makarantu 720 da kungiyar OEQA ta ziyarta sun bi umarnin komawa ranar 4 ga watan Junairu, 2022, wanda gwamnatin jihar Legas ta gindaya mata, wanda hakan ke nuni da cewa an biya kusan kashi 89 cikin dari.
“Duk da cewa abin yabawa ne yadda makarantun suka bi umarnin ranar da jihar ta koma aiki, amma abin takaici ne yadda kusan makarantu 80 suka kasa cika umarnin. Mun fitar da wasiku tare da sanya allunan rashin bin ka’ida a ƙofofin waɗannan makarantun da suka ki bin umarnin.”
Seriki-Ayeni ta kara da cewa gwamnati ba za ta rufe duk wata makarantar da ta ki bin umarnin ba.
“Don kaucewa shakku, gwamnatin jihar Legas ba ta rufe wata makaranta ba kuma ba za ta rufe ba, domin hakan ba zai yi tasiri ga koyo ba.
“Kamar yadda muka saba yi a baya, gwamnatin jihar na fatan bin doka kuma za ta ci gaba da tattaunawa da dukkan makarantu kan al’amuran da suka shafi ci gaban ilimi a jihar,” inji ta.