By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnatin jihar Legas tace za a yi wa mutane kusan 400 dake fama da nakasa magani kyauta.
Babban sakatare na ma’aikatar lafiya ta jihar Legas, Dr Olusegun Ogboye ne ya bayyana haka a ranar Litinin a lokacin daya ziyarci wurin tantance sabbin mutanen da suka amfana a asibitin koyarwa na jami’ar jihar Legas.
Yace aikin tiyatar gyaran an yi niyya ne domin farfado da mutane musamman yaran dake fama da nakasar kafafu dake shafar lafiyar girmansu na yau da kullun.
A cewarsa, atisayen ya samu sama da mutane 400 da zasu ci gajiyar shirin, wadanda za a tantance su na tsawon kwanaki biyu, inda za a gudanar da gwajin lafiyar daya dace.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa yara 80 ne dai zasu ci gajiyar aikin tiyatar gyaran fuska yayin da wasu za a ba su ilimin motsa jiki, abinci mai gina jiki da kiwon lafiya da kuma na’urorin motsa jiki na taimakawa.
Kazalika yace “Tsarin ya kunshi tantancewa inda likitocin fida ke duba marasa lafiya tare da zabar wadanda suka cancanci cin gajiyar aikin tiyatar da sauran wadanda za su iya amfana da na’urorin taimako da sauran nau’ikan gyaran jiki.”
Jami’in kula da shirin, Dokta Tolulope Ajomale ya bayyana cewa sama da majinyata 6,000 ne suka ci gajiyar shirin tun lokacin da aka fara shi.
Ajomale yace shirin ya rikide zuwa wani shiri na wayar da kan jama’a na tiyata da yawa wanda ke binciko aikin tiyata, jiyya da na’urorin motsa jiki masu taimakawa wadanda ke inganta sakamakon lafiya.