By Abbas Yakubu Yaura
A ranar Litinin wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta sallami tsohon ministan ayyuka na musamman da harkokin gwamnati Kabiru Turaki, tare da wanke shi daga zargin karkatar da kudade.
DUBA WANNAN LABARIN: An Tsare Wasu Jami’an Sojoji Hudu Na Bogi Da Laifin Aikata Fashi A Jihar Osun
Mai shari’a Inyang Ekwo, a hukuncin da ya yanke kan rashin shigar da karar da hukumar ta shigar, ya ce hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC) ta kasa alakanta Turaki da wadanda ake tuhuma da laifukan da ke kunshe cikin tuhume-tuhume 16.
Ya ce masu gabatar da kara ba za su iya kafa hujja da su ba.
Mai shari’a Ekwo ya ce wadanda ake tuhumar sun kori dukkanin shaidun da masu gabatar da kara suka gabatar a kan lamarin a lokacin da ake yi musu tambayoyi, inda ya bayyana shaidu 12 da EFCC ta dogara da su a matsayin shedu.
Alkalin ya ce an kafa shi ne a lokacin da ake yi masa tambayoyi cewa Turaki bai sanya hannu a asusun ma’aikatar ba kuma bai bayar da izinin biyan ko wani kudi ba.
Ya yi daidai da hujjar cewa tsohon ministan ba mamba ne a kwamitin kula da kwangilar ministoci ba kuma babu wani kudade da aka samu daga asusun ma’aikatar zuwa kamfanin Turaki.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa hukumar EFCC na tuhumar tsohon ministan da wasu mutane da laifin almundahana naira miliyan 715 ba bisa ka’ida ba.
(NAN)