Hukumar zabe mai zaman kanta ta bukaci ‘yan Najeriya da su guji wasu bata gari da kanyi amfani da bukatar da mutane ke da ita, wajen zambar su.
Hukumar INEC din ta ce akwai yanzu haka wasu masu zamba dake fakewa da guzma wajen Harbin Karsana, ta hanyar cewa zasu yiwa mutane katin zabe duk kuwa da cewa an kammala yin rijistar yanzu haka.
A wata sanarwa da kwamishinanta na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu kada kuri’a, Festus Okoye ya fitar a ranar Litinin, ya ce masu yin rijistar zaben da sunan su, basu da amincewar INEC.
DUBA WANNAN KARIN LABARIN: Sanatoci da dama sun goyi bayan tsige Buhari
A cewar hukumar, ikirarin cewa gwamnatin tarayya ta amince da yin rijistar katin zabe ta hanyar yanar gizo don kaucewa cunkoson jama’a a cibiyoyin NIMC karya ne.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Bayan sa’o’i 24 da dakatar da rajistar masu kada kuri’a, aka fara jawo hankalin hukumar zabe mai zaman kanta a wani shafin yanar gizo da ke kira ga ‘yan Najeriya da su yi rajistar katin zabe (PVC) da ke ikirarin cewa gwamnatin tarayya ta amince da shi.
“An shawarci jama’a da su guji fadawa hannun ‘yan damfara ta yanar gizo kuma su guji irin wadannan shafuka na bogi.
“Hukumar ta kammala ci gaba da gudanar da rijistar masu kada kuri’a a fadin kasar baki daya, kuma ba ta bukatar bude wani karin shafi ko tashoshi domin yin rajistar masu zabe.”